Rikici ya ɓarke tsakanin jami’an DSS da ma’aikata a zauren majalisar tarayya da ke Abuja.
Lamarin ya faru ne a jiya Juma’a lokacin da jami’an DSS ke kan aiki suka hana wasu manyan ma’aikata biyu wucewa lamarin da ya kai su da fara hayaniya, wanda ya ja hankalin sauran ma’aikata
Daga bisani baturen yansanda na cikin majalisar da mataimakiyar magatakardan majalisar dattawa suka shawo kan lamarin
Shedan gani da ido yace Rikicin ya fara ne lokacin da jami’an DSS da ke gadin ƙofar suka nemi wasu manyan ma’aikatan NASS biyu su bayar da katinsu na shaida kafin su wuce.
Ganau ba jiyau ba ya tabbatar da cewa jami’an biyu, John Nnadi mai aiki da kwamitin mai na majalisar dattawa da mataimakin darakta, Chris Odoh, sun nuna wa jami’an katinsu.
A cewarsa duk da sun nuna wa jami’an DSS katin shaidarsu amma suka tsayar da su bisa zargin cewa ba su gabatar da kansu yadda ya kamata ba.
A matsayinsu na manyan ma’aikatan NASS, sun yi yunƙurin shiga ɓangaren White House amma jami’an DSS suka hana su, lamarin da ya haddasa hatsaniya.
Duk wani yunƙuri da masu wucewa suka yi domin sasanta rikicin bai cimma nasara ba, sai da jami’an DSS suka fara cin mutuncin ma’aikatan, suka wuce da su Ofis.
Yadda jami’an tsaron suka ɗauki mutanen biyu da tsiya- tsiya zuwa ofishinsu na cikin majalisar, wanda bai wuce nisan mita 125 ba shi ne ya jawo hankalin sauran ma’aikata.
Sai dai DPO ya shawo kan lamarin A fusace ma’aikatan majalisa suka cika ƙofar ofishin DSS kuma suka yi barazanar cewa za su ɗauki tsattsauran mataki matuƙar ba a saki waɗanda aka kama ba, cewar Daily Trust.
Shugaban ƴan sandan majalisa (DPO), Alex Annagu, da mataimakiyar magatakar majalisar dattawa, Misis Ilobah Isabella, sun hanzarta zuwa wurin domin shawo kan lamarin.












