Ana rade-radin fadar shugaban kasa ta fara yunkurin sauya Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyar APC na kasa.
Yunkurin ya biyo bayan kiraye-kiraye da masu ruwa da tsaki da tsagin jam’yyar suka yi kwanakin baya a Najeriya.
Jaridar Leadership ta binciko cewa fadar shugaban kasa ta na kokarin kafa kwamitin da za su nemo wanda zai rike muƙamin bayan sauke Ganduje.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnonin jam’iyyar APC da ke yankin Arewa ta tsakiya ne za a daura wa alhakin nemo wanda zai maye gurbin Ganduje.
Har-ila-yau jam’iyyar ta ayyana cewa shugaban ta a wannan karon zai fito ne daga yankin Arewa ta tsakiya. Bangaren da sabon shugaban APC zai fito
Sai dai wasu bayanan da suka fito daga fadar shugaban kasa sun nuna cewa sabon shugaban zai fito ne daga ɓangaren CPC, cewar jaridar Nigerian Bulletin.
CPC tana cikin jam’iyyun adawa da suka yi haɗaka wajen kafa jam’iyyar APC gabanin zaben 2015.
Korafin da aka yi kan Ganduje a APC Daga cikin abubuwan da aka koka kan Ganduje akwai matsalolin da jam’iyyar ta samu a zabukan fitar da gwani a jihohin Edo da Ondo.
A wani bangaren kuma ana rade-radin cewa shirin dawowar Rabi’u Musa Kwankwaso jam’iyyar APC na daga cikin abubuwan da suka sa za a sauke Ganduje.
Ganduje ya ce APC ce mafita a Najeriya A wani rahoton, kun ji cewa duk da matsalar da shugaban APC ke ciki, ya tabbatar da cewa jam’iyyarsu ita ce kadai hanyar dakile matsalolin kasar.
Abdullahi Ganduje ya tabbatar da haka ne a lokacin da ya je jihar Gombe domin ayyukan cigaba inda ya ce APC ce kadai mafita a Najeriya.












