Babban Sufeton ‘Yan sandan Najeriya ya ba da umarnin taƙaita zirga-zirgar duk wani nau’in abin hawa a kan tituna da ruwa da sauran hanyoyin sufurin ƙasar tun daga karfe 12 na daren jajiberen zaɓe.
Usman Alƙali Baba, ya ce an ɗauki matakin ne don tabbatar da yanayi mai inganci, tsaro da aminci ga harkokin zaɓen da za a yi a faɗin ƙasar.
Sanarwar ta kuma yi matsananci gargaɗi ga dukkan jami’an tsaro su guji raka mutanen da suke karewa da ‘yan siyasa rumfunan zaɓe.
Sanarwar ta ce umarnin taƙaita zirga-zirgar, na da nufin tabbatar da yanayin kwanciyar hankali da aminci ga masu zaɓe.
Sanarwar ta kuma ambato Babban Sufeton ‘Yan sandan Najeriya Usman Alƙali Baba yana gargaɗin duk jami’an tsaro su guji raka iyayen gidansu da ‘yan siyasa rumfunan zaɓe da cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe don kuwa duk wanda aka kama ya saɓa wa umarnin zai fuskanci hukunci mai zafi.












