Jadawalin maniyyata daga jihohi
Kaduna — 4,656
Sokoto — 3,563
Kebbi — 3,344
Niger — 3,200
Kwara — 3,100
Kano — 2,906
Katsina — 2,654
FCT — 2,489
Bauchi — 2,290
Nasarawa — 1,866
Lagos — 1,857
Borno — 1,780
Adamawa — 1,767
Zamfara — 1,596
Osun — 1,548
Plateau — 1,345
Yobe — 1,290
Gombe — 1,262
Jigawa — 1,260
Oyo — 1,047
Taraba — 1,000
Ogun — 925
Ondo — 491
Edo — 265
Ekiti — 186
Imo — 98
Benue — 87
Rivers — 42
Delta — 40
Enugu — 18
Bayelsa — 13
Ebonyi — 13
Kogi — 13
Sojoji — 403
Bisa la’akari da jadawalin da ke sama, Najeriya na da yawan maniyyata 48,414 a shekarar nan ta 2024, sabanin a baya inda ko a 2023 ‘yan Najeriya fiye da dubu 90 ne suka halarci aikin hajjin bara.
Ana dai alakanta raguwar yawan jama’ar da tsadar farashin kujerar aikin na bana da ta ninka na bara fiye da sau biyu.
To sai dai za a iya cewa babu tabbacin cewa gabadayan maniyyatan fiye da dubu 48 na Najeriya ka iya halartar aikin hajjin bana sakamakon ba kowa ne zai iya cika kudin da hukumar alhazan ta nemi a cika duk kuwa da cewa wasu jihohin sun cika wani kaso na kudin.
Yanzu dai za a iya cewa alkaluman da hukumar alhazai za ta fito da su ne kawai ka iya zama abin dogaro dangane da sanin hakikanin yawan mutanen da za su halarci aikin hajjin na 2024.










