• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kano Ta Bankado Wasu Unguwanni Guda 68 Da Ake Ginawa Ba Bisa Ka’ida Ba

aksam by aksam
February 28, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA

Hukumar tsara Birane ta Jihar Kano, KNUPDA, ta gano wasu sabbin rukunonin unguwanni 68 da aka samar da su ba bisa ka’ida ba, biyo bayan binciken da ake yi na tsaftace birnin daga gine-ginen da ake yin su ba bisa ka’ida ba.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Don tabbatar da cewa ana bin ka’idojin gine-gine a jihar kano, gwamnatin jihar ta kafa kotuna domin hukunta wadanda ke sana’ar yin gine-gine ba bisa ka’ida ba, tare da hukuncin daurin watanni shida a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Shugaban Hukumar ta KNUPDA ta jihar kano, Arc. Ibrahim Yakubu Adamu, ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a Ofishinsa dangane da aiyukan kwamitin da ya kafa.

Ibrahim Yakubu Adamu, ya bayyana cewa daga cikin masu rukunonin unguwanni (layout) 68 din da aka gano suna ginin ba bisa ka’ida ba, masu guda 40 sun amsa gayyatar da kwamitin yayi musu, yayin da wasu suka ki girmama gayyatar da akai musu.

Ya ce, “Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ba mu cikakken ikon gudanar da ayyukan mu tare da tabbatar da cewa mun tsaftace jihar daga yawaitar gine-ginen ba tare da tsari ba, kuma duk wanda aka samu yana karya doka to tabbas za a hukunta shi.”

Adamu ya bayyana cewa gwamnati ta sake farfado da wata doka da ake da ita a shekarar 2011, wacce ta baiwa hukumar cikakken ikon kamawa tare da hukunta duk wanda ya karya dokar tsara birane da yin gine-gine ba bisa ka’ida ba .

Sai dai kuma ya ce domin kawo karshen yin gine-gine ba bisa ka’ida ba a fadin jihar, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya amince da gina sabbin burane guda biyu wadanda za su kunshi dukkan wasu kayan more rayuwa da ake bukata.

Ya yi gargadin cewa ofishinsa “zai yi aiwatar da dokokin tilastawa duk wanda ya ki bin umarnin kan daina yanka filayen awon igiya da kuma yin gini ba tare izinin hukumar ba, kuma kada ku manta cewa hukuncin zaman gidan yari na watanni 3 ko watanni 6 ne akan wanda aka samu da laifin ba tare da zabin binyan tara ba”.

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Zargin rashin sanin makamar aiki na kara girmama kan gwamnan CBN

Next Post

Kasar Chadi ta sanar da lokacin da zata gudanar da zabe dan Komawa tafarkin demokradiyya

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Die Rolle von RNG in n1bet casino Spielen

April 22, 2025
Cikakken bayani kan Dalilan da su ka sanya Ganduje yin murabus a mukaminsa

Cikakken bayani kan Dalilan da su ka sanya Ganduje yin murabus a mukaminsa

June 27, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media