Yadda Muka Yi Kutun-Kutun Don Yin Waje da Adamu, Omisore, daga shugabanci jam’iya wani jigo a APC
Tsohon darakta janar na kungiyar gwamnonin APC, Salihu Lukman, ya yi karin haske game da al’amuran jam’iyyar APC mai mulki.
Jigon na APC wanda ya bukaci Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya bari sassa da tsarin jam’iyya mai mulki su yi aiki, ya yi bayani kan yadda tsohon shugaban jam’iyyar na kasa ya bar jam’iyyar.
Lukman, tsohon mataimakin shugaban APC, ya bayyana hakan ne a wani shirin Channels TV
Ya ce wasu jiga-jigai sun yi ruwa sun yi tsaki wajen tsige Sanata Abdullahi Adamu da Sanata Iyiola Omisore a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa da sakataren jam’iyyar a watan Yulin 2023.
Sai dai kuma, Lukman ya bayyana cewa ya kamata a farfado da APC ta yi aiki bayan ficewar Adamu da Omisore.
“Muhimmin batu wanda shi ne abin da nake sa rai daga shugaban kasa Asiwaju shine tabbatar da cewa tsarin jam’iyyar mu yana aiki.
“Bacin raina bayan mun yi yakin fitar da Abdullahi Adamu da Sanata Iyiola Omisore daga shugabancin jam’iyyar, ba wai fitar da su ba ne.
“A’a shine batun daukar matakan da suka dace don ganin cewa wadannan tsare-tsare suna aiki ta yadda duk wanda ya zo zai samu damar yin aiki bisa tsarin mulkin jam’iyya.”












