Jam’iyyar PDP ta yi kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ziyarci wurin da wasu ƴan bindiga suka kashe ƴan Najeriya a jajibirin Kirsimeti a yankin Bokkos da Barkin Ladi na jihar Plateau.
Shugaban masu sa ido kan zaman lafiya na al’umma a ƙaramar hukumar Bokkos, jihar Plateau, Kefas Mallai, ya bayyana cewa ƴan bindigan sun kashe sama da mutum 150.
Tinubu, a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara ta musamman kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Talata, ya yi Allah wadai da hare-haren tare da bayar da umarnin farautar waɗanda suka kai harin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu aksamedia84@gmail.com
A martanin sa, sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na ƙasa, Debo Ologunagba, ya yi tambaya kan abin da ya jawo gazawar bayanan sirri kafin da kuma lokacin da aka kai harin.











