An fara yaɗa jita-jita da rahotanni kan yiwuwar juyin mulki ko kuma wani gagarumin bore a kasar Ivory Coast, musamman a birnin Abidjan, inda aka rika jin karar harbe-harbe.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa rahotannin da ke fitowa daga kafofin sada zumunta na nuni da cewa rikici na kunno kai cikin sauri a kasar.
Rahotanni sun ce akalla mutane 33 ne aka kashe a cikin sa’o’i 48 da suka gabata, yayin da ake ci gaba da gwabza fada a wasu sassa na babban birnin kasar, Abidjan.
Sai dai har yanzu babu tabbacin wannan rahoto a hukumance, saboda an ce an katse hanyoyin sadarwar intanet, kuma babu wasu bayanai daga gwamnati.
Wasu majiyoyi na ikirarin cewa shugaba Ouattara ya yi ɓatan-dabo, ko kama shi, ko kuma ya mutu, amma babu wata sanarwa a hukumance daga gwamnati game da haka.











