A yammacin ranar Talata ne jami’an tsaro sun tsare dan Majalisar a Filin Jirgin Sama na Malaman Aminu Kano, a yayin da yake kan hanyarsa tazuwa Abuja.
Hakan kuwa na zuwa ne bayan kwanaki kadan da cin zabensa na komawa kan kujerarsa, a zaben da ake alakantawa da tashe-tashen hankula.
Jam’iyyar NNPP ta zargi dan majalisar da hannu a harin da aka kai a ofishinta na Karamar Hukumar Doguwa, inda aka kashe wasu mutum biyu da aka kone su da ransu.












