Daga: Hassan Umar Gwammaja
Takardar gayyata wate ki kira da Saekin ya halarci wani bincike da za a gudanar a Headkwatar dake Abuja dangane da matsallar da ta faru a lokacin bukukuwan Sallah
Wasikar, wadda ke dauke da kwanan wata 4 ga Afrilu, 2025, ta bayyana cewa za’a gudanar da taron binciken ne a ranar Talata, 8 ga Afrilu, 2025 da karfe 10:00 Na Safe a Sashin Leken Asiri
A cewar takardar, an bukaci Mai Martaba Sarkin Muhammadu Sunusi da ya bayyana a ofishin ta domin tattaunawa da bayani kan wani abin da ya faru cikin Masarautar ta Kano ya yin gudanar da bukukuwan Sallah. Takardar na dauke da sa hannun CP Olajide Rufus Ibitoye, kwamishinan ‘Yansanda mai kula da sashen leken asiri.












