DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 23 ciki har da basarake mai daraja ta biyu da fadawansa a karamar hukumar Yorro ta jihar Taraba.
Lamarin ya afku ne a daren ranar Talata inda ‘yan bindigar masu yawan gaske suka shiga garin tare da kewaye shi.
Wani mazaunin garin ya shaida wa BBC cewa, ba su san adadin ‘yan bindigar da suka shiga garin ba saboda yawansu.
Ya ce,” sun shiga cikin dare suka dauki na dauka suka bar na bari, kuma a cikin wadanda suka dauka baya ga basaraken da dogarinsa, akwai limamin masallacin Jumma’a da fastoci biyu da kuma sauran jama’ar gari.”
Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun fasa shaguna tare da satar kayan abinci da abubuwan sha.
“Ba wannan ne zuwan su na farko ba, wannan shi ne karo na hudu da suka je garinmu” In ji mazaunin garin na.
Tuni dai rundunar ‘yan sandan jihar ta Taraba ta ce ta fara bincike tare da neman mutanen da aka sace.












