Yan sanda a kasar India sun saki wata tantabara bayan tsare ta na tsawon watanni takwas bisa zargin cewa yar leken asiri ce daga kasar China.
Yan sandan na kasar Indiya reshen jihar Mumbai sun tsare tattabarar ne tun a watan Mayu bayan ganin ta da zobe guda biyu a kafarta kuma zobbinan dauke da rubutun Chinanci, kuna aka gano karamar na’ura a daya daga cikin zoben, kamar yadda jaridar UPI news ta wallafa.
Yan sanda masu bincike sun tsare ta a asibitin Bai Sakarbai Dinshaw na Dabobi kan zargin yin ayyukan leken asiri a madadin China.
Bayan zurfafa binciken da ‘yan sanda suka yi ya sun gano tare da tabbatar da cewa tantabarar ba yar leken asirin China bace, amma ya shiga gasar tseren ruwa ne a Taiwan kuma ya kauce hanya, ya kare a Indiya.
Kungiyoyin kare hakkin dabobi PETA Indiya ta yi maraba da sakin tantabarar da ta dade tana kiraye-kirayen a saki.
Meet Ashar, shugaban sashin yaki da cin zalin dabobi na kungiyar, cikin wata sanarwa da ya fadawa New York Times ya ce:
“PETA India na samun kiraye-kirayen neman daukin gaggawa na dabobbi fiye da 1,000 duk mako, amma wannan ne karon farko da aka samu batun sakin wanda ake zargin dan leken asiri ne.”











