Anbukaci Al,umar musulmin duniya dasuci gaba da taya kasar falasdin da Addu’oin bisa yadda take tsaka mai wuya bayanin hakan yafitone tabakin.
Ambassador Abdullah Bin shawesh na kasar falasdin
A wata ziyara dayakawo jahar kano domin A tayasu da Addu’oin samun sauki akan yadda kasar israila take kashemusu mutane .
Yabai yana hakanne yayin taron da,awa da kungiyar mata musulmi ta Amwa.tashirya yau juma,a taron dai ya gudana ne A masallacin Afdul waham kulafau,rashidin dake unguwar sharada kwanar ganduje.
Yace duba da yadda alakar kasarsu da Nigeria tasa suka gadacewar zuwansu domin su sanar da al,ummar Nigeria halin da suke ciki .
Itama anata bangaran shugabar mata musulmai ta africa wato Amwa. Hajiya Aisha Ishak sulaiman. tace zasucigaba data yasu da Addu’oin samun sauki domin suna takaicin irin cinzarafin da akewa yan uwansu mata awannan yakin tace zuciyarsu takadu matuka da yadda sukaji irin batutuwan da yazo dasu .
inda ta kara dacewa sunanan suna kakari wajan dada fadakar da al,umma akan batun domin kuwa akwai wadanda suke yiwa abum wani irin kallo.
Hakazilika itama anata bangaran Saanatu Ala kurawa jagora atafiyar da Awa anan kano tace daga wannan sun lashi takobin wayar dakai ga jama,a ako ina acikin kasarnan.tace wannan bakaramin zalumcibane ga musulmai .inda takara dacewa du wani musulmi dan uwan musulmi ne ako ina .
Daga karshe ta yikira ga kafafen yada labarai da suzama masu yadda labarin gaskiya akowane lokaci duba da yadda wasu kafafen suke yada labaran shamcin gizo akan wannan yakin .
Suma anasu bangaran wadanda suka samu halartar wannan taron sunbaiyanamana gamsuwar su da wannan taron inda sukace kuma za suyi amfani da wannan fadakarwar ta hanyar da yadace dakuma saka yan uwansun musulmai acikin Addu’oin su akoyaushe.












