Ƙungiyar Likitoci ta Najeriya ta ce fiye da rabin likitocin ƙasar ne ba su sabunta lasisinsu ba a shekara ta 2023, abin da ke nufin mai yiwuwa ko dai sun tsallake sun bar ƙasar ko kuma sun canza sana’a.
Shugaban ƙungiyar Farfesa Bala Audu ya ce a shekarar da ta wuce likitoci kimanin 50,000 ne kawai suka sabunta lasisin aikinsu, a cikin adadin likitoci kimanin 130,000 da ake da su a Najeriya.
Ya ce likitoci a Najeriya suna aiki kusan tsawon sa’a 24 a mafi yawan lokuta saboda yawan aiki, kuma ba tare da an ƙara musu haƙƙoƙin aiki gwargwadon aiki da sadaukarwar da suke yi ba.
Farfesa Bala Audu ya ce likita ɗaya a Najeriya yana duba kimanin mutum 6,000, ninki goma na abin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta ƙayyade na likita ɗaya ya duba mutum 600.
A cewarsa, irin wannan yawan aiki na taɓa lafiya da ƙwazon aikin likitocin Najeriya, inda a baya-bayan nan har aka samu wani likita da ya rasu saboda suƙewar aiki.











