Lamarin jimami da ya afku a ranar Alhamis a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Jihar Kano, inda aka tsinci gawar wata daliba mai suna Aishat Yahaya Olabisi a wani gidan da take zaune a wajen jami’ar ya dugunzuma dalibai da dama
Tun da fari dai an tsinci gawar dalibar jami’ar Aliko Dangoten ne mai suna aisha Yahya Olabisi wacce take aji uku a fannin fasahar abinci da kimiyya bayan ta dawo dakinta daga makaranta
Daya daga cikin daliban da ta zanta da jaridar Punch a ranar Asabar ta dora laifin rasuwar dalibar da matsin jarrabawa.
A cewarta: “Lafiyarta kalau kafin ta tafi rubuta jarrabawarta ta farko a zangon farko da ake gudanarwa.
” Sai dai, bayan jita-jitar da aka yada cewa dalibar ta rasu ne a dakin karatun da ke cikin jami’ar, tuni mahukunta a jami’ar suka fayyace komai a Bayanin da jami’ar Aliko Dangote ta fitar
A wata sanarwar da shugaban kula da harkokin dalibai na jami’ar, farfesa Abdulkadir Dambazau ya fitar a ranar 3 ga watan Mayu, ya ce ba a cikin jami’ar ta rasu ba.
Ya kuma bayyana matakan da jami’ar ta dauka na binciken inda dalibar take bayan rashin ganinta, inda daga baya aka gano ta mutu a dakinta.
I zuwa yanzu, an dauki gawar Aishat zuwa asibitin koyarwa na Aminu Kano da ke birnin Kano don zurfafa bincike akan gawar.
Kazalika an tsince gawar wata daliba a Jami’ar UNIPORT ta jihar Rivers
An tsince gawar dalibar jami’ar ne a jihar Rivers a cikin dakinta.
Lamarin ya tada hankalin jama’ar, yankin inda tuni aka fara binciken sanadiyyar mutuwarta tare da daukar mataki.
A cewar majiyar mu, dalibar ta mutu a dakinta da ke wajen makaranta bayan ta dawo daga karatu. Asali: Legit.ng












