Kwamrad Toyin Raheem ya shawarci Bola Ahmed Tinubu da ya yi murabus daga matsayin shugaban kasa
Raheem ya bayyana halin da tattalin arzikin Najeriya ke ciki a yanzu da kuma garkuwa da mutane da ake yi don kudin fansa a matsayin dalilinsa na bukatar hakan
Jaridar Legit ta ruwaito cewa ‘yan Najeriya na fuskantar yawancin kalubalen da jam’iyyar Shugaban kasa Tinubu, APC ta yi alkawarin magancewa shekaru tara da suka gabata
Da yake zantawa a wata hira da Sahara TV, Raheem ya ce gwamnatin Tinubu, ta gaza duk da cewar watanninta tara kacal akan mulki.
Ya kuma nuna rashin jin dadinsa kan annobar garkuwa da mutane a kasar, inda ya ce a yanzu masu garkuwa da mutane suna shiga gidaje su kai hare-hare.
“Ba tare da fadin kalamai a kaikaice ba, kamar dai Najeriya ta gaza a matsayin kasa.
“Wannan gwamnati mai ci, ta gaza ba tare da la’akari da yawan watannin da ta yi akan mulki ba. Ba gazawa kawai ba, face mugun gazawa.
“Da haka kawai ne, mutum zai yi tsammanin ganin shugaban kasar ya yi murabus zuwa yanzu, saboda alamu sun nuna ba shi da maganin matsalar kasar nan.
“Me muke magana akai? Kamar dai ba mu da wata gwamnati a halin yanzu. Wannan ita ce gaskiyar magana.”











