• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sanya Dokar-Ta-Baci Kan Yunwa Da Rashin Tsaro a Najeriya

aksam by aksam
May 2, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Daga Hassan Umar Gwammaja

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana matsalar yunwa, fatara da rashin tsaro a matsayin manyan matsalolin da ke bukatar kulawa ta gaggawa, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da za a ɗauki tsauraran matakai domin magance su a faɗin ƙasar nan.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, wanda ya wakilce shi a bikin Ranar Ma’aikata ta Duniya ta 2026 da aka gudanar a Eagle Square da ke Abuja.

A cewarsa, rashin tsaro na hana manoma komawa gonaki yadda ya kamata, lamarin da ke rage yawan amfanin gona tare da ƙara jefa al’umma cikin yunwa da fatara.

Ya ce matsin tattalin arziki da hauhawar farashi sun ƙara tsananta rayuwar ‘yan Najeriya, don haka gwamnati ta ɗauki wannan lamari a matsayin abin da ya dace a ba fifiko cikin gaggawa.

Shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa ta fara aiwatar da matakai daban-daban da suka haɗa da ƙarfafa tsaro, rage talauci, da samar da ayyukan yi musamman ga matasa domin rage zaman kashe wando da inganta rayuwar al’umma.

Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnati na shirin samar da guraben aiki ga matasa 45,000 domin taimakawa wajen ƙarfafa tsaro da tabbatar da zaman lafiya a sassa daban-daban na ƙasar.

Tinubu ya ƙara da cewa haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro da ƙungiyoyin ma’aikata na da matuƙar muhimmanci wajen shawo kan matsalolin da suka addabi Najeriya.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Zai Yi Balaguron Mako Biyu Zuwa Faransa, Kenya Da Ruwanda

Next Post

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Hukumar Zabe Ta Kasa Mai Zaman Kanta A Najeriya Ta Ayyana Sakamakkon Zaben Jihar Imo

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta A Najeriya Ta Ayyana Sakamakkon Zaben Jihar Imo

November 12, 2023
Yadda Shugabancin tashar Kano line ke fafutuka wajen gamsar da abokan huldar sa

Yadda Shugabancin tashar Kano line ke fafutuka wajen gamsar da abokan huldar sa

November 16, 2023
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media