Daga Hassan Umar Gwammaja
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana matsalar yunwa, fatara da rashin tsaro a matsayin manyan matsalolin da ke bukatar kulawa ta gaggawa, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da za a ɗauki tsauraran matakai domin magance su a faɗin ƙasar nan.
Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, wanda ya wakilce shi a bikin Ranar Ma’aikata ta Duniya ta 2026 da aka gudanar a Eagle Square da ke Abuja.
A cewarsa, rashin tsaro na hana manoma komawa gonaki yadda ya kamata, lamarin da ke rage yawan amfanin gona tare da ƙara jefa al’umma cikin yunwa da fatara.
Ya ce matsin tattalin arziki da hauhawar farashi sun ƙara tsananta rayuwar ‘yan Najeriya, don haka gwamnati ta ɗauki wannan lamari a matsayin abin da ya dace a ba fifiko cikin gaggawa.
Shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa ta fara aiwatar da matakai daban-daban da suka haɗa da ƙarfafa tsaro, rage talauci, da samar da ayyukan yi musamman ga matasa domin rage zaman kashe wando da inganta rayuwar al’umma.
Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnati na shirin samar da guraben aiki ga matasa 45,000 domin taimakawa wajen ƙarfafa tsaro da tabbatar da zaman lafiya a sassa daban-daban na ƙasar.
Tinubu ya ƙara da cewa haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro da ƙungiyoyin ma’aikata na da matuƙar muhimmanci wajen shawo kan matsalolin da suka addabi Najeriya.












