Rundunar Sojojin Najeriya ta sanar da kashe a kalla mutane 86 da ake zargin ’yan bindiga ne tare da kama wasu 101 a wasu hare-hare a fadin kasar a cikin makon da ya gabata, kamar yadda Rundunar ta bayyana .
Edward Buba, kakakin rundunar sojin Najeriya, shi ne ya shaidawa manema labarai hakan a babban birnin tarayya Abuja ya ce farmakin da sojojin suka gudanar ya mayar da hankali ne kan fatattakar sansanonin ’yan ta’adda daga sama, sannan kuma sun ba da karfi sosai a yankunan da ’yan ta’addan ke fakewa.
Buba ya ce rundunar sojin sun kuma sako wasu da dama da aka yi garkuwa da su.











