Daga Hassan Umar Gwammaja
Wata majiya ta bayyana cewa, sarkin ya tafi wata ziyarar aiki a Abuja domin halartar wani babban taro da ya kunshi sarakuna.
Majiyarmu ta ruwaito cewa Aminu Ado Bayero ya koma Kano kwanaki kadan bayan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sauke shi daga kan karagar, kuma tun a wancan lokaci yake Kalubalantar cire shin a gaban Kotu.
Tun ranar 20 ga watan Yuli da sarkin ya halarci taron yiwa kasa addu’o’in samun zaman lafiya a gidan Marigayi Sheikh Ishaq Rabi’u dake goron Dutse, sarkin bai sake fita ba sai wannan rana ta juma’a da ya fita zuwa ban-ban birnin tarayya Abuja.
An hango Aminu Ado Bayero a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja tare da Oni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi, da dai sauransu.












