DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Wani malamin makarantar mai suna Sani Abdullahi wanda ya kubuta ya bayyana cewa ɗalibai 287 ne aka sace a makarantar.
Sani Abdullahi ya ce “A bangaren sakandare ɗalibai 187 ne suka bace amma bangaren firamare ɗalibai 125 da farko ba a gansu ba amma daga bisani guda 25 sun dawo.”
Malamin wanda ya bayyana hakan lokacin da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya ziyarci makarantar domin gani da ido yadda lamarin yake , ya kara da cewa “na shigo makaranta misalin karfe 7:45 sai na shiga ofishin principal kuma sai ya ce min in waiga baya, ina juyawa sai naga ‘yan bindiga sun kewaye makarantar”.
“Mun ruɗe bamu san inda zamu ba, kafin da suka tafi damu daji sai muka canza hanya,” in ji Sani Abdullahi.
Malamin makarantar ya ce ‘yan bindigar sun kashe mutum daya.
Yaran da lamarin ya rusta da su shekarunsu sun kama ne daga takwas zuwa 15.
Ya bayyana cewa ana cikin wani hali na fargaba tun bayan sace daliban a safiyar Alhamis.
Wani da ya shaida faruwar lamarin ya ce “Babu wani gida a Kuriga wanda wannan abin bai shafe shi ba”.












