Ƙasar Pakistan ta fitar da sanarwa a hukumance inda ta yi kakkausar suka kan hare-haren da aka kai kan cibiyoyin makamashi a Jubail, tare da bayyana goyon bayanta ga al’ummar Saudiyya. Ta ce irin wadannan hare-hare a kan Saudiyya na raunana zuciyar daukacin al’ummar Musulmi.
A baya-bayan nan kuma, Pakistan ta gargadi kasashen Musulmi da kada su fada cikin abin da ta kira ajandar Isra’ila.












