Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amincewa gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin gwamnan Kano .
Idan za’a iya tunawa a makon da ya gabata ne gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya mikawa majalisar sunan Murtala Sule Garo domin tantance shi ta kuma Amince masa ya nada shi a kujerar mataimakin gwamna Kano .
Kadaura ta rawaito a Ranar 27 ga watan mayu, 2026 ne tsohon mataimakin gwamnan Kano Aminu Abdussalam Gwarzo ya ajiye mukaminsa bayan wata rashin jutuwa da suka samu da Gwamna saboda ya gaza binsa zuwa jam’iyyar APC da ya koma.
Majalisar dokokin ta Kano dai ta Amince da Murtala ne bayan da kwamitin da ta nada karlashin jagoranci mataimakin shugaban majalisar Hon. Muhammad Bello Butu-butu ya gabatar da rahotonsa.
Kwamitin tantancewa na Majalisar Dokokin Jihar Kano ya bayyana cewa ya yi cikakken nazari kan takardun karatun Murtala Garo, kwarewarsa a aiki da kuma tarihin rayuwarsa, bisa tsarin tantancewar da majalisar ke bi.
Bayan tattaunawa kan rahoton kwamitin, ‘yan majalisar sun amince baki daya da shawarwarin da aka gabatar, inda suka tabbatar da Garo a matsayin wanda ya cancanta kuma ya dace ya zama Mataimakin Gwamnan Jihar Kano.
Daga nan ne Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Ismail Falgore, ya sanar da amincewar majalisar, lamarin da ya baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf dama domin rantsar da Garo a matsayin sabon mataimakin gwamna.












