An shigar da ƙorafi mai ƙarfi kan hukumar EFCC bisa tuhumar da take yi wa tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello
Tun bayan da ya bar ofis bayan kammala wa’adinsa na shekara takwas, hukumar ta sa ido kan tsohon gwamnan
A halin da ake ciki, ƙungiyar Kogi In Diaspora Association (KIDA) ta caccaki hukumar EFCC bisa rashin adalcin da ta yi wa tsohon gwamnan
Jaridar Leadership ta ce a wata wasiƙa mai dauke da kwanan watan 9 ga watan Fabrairun 2024, zuwa ga ƙungiyoyi daban-daban na ƙasa da ƙasa, mai ba da shawara na ƙungiyar, Seyi Olorunsola, ya bayyana damuwarsu tare da neman a shiga tsakani.
Wasiƙar, wacce aka rabawa manema labarai a Abuja a ranar Asabar, 10 ga watan Fabrairu, ta yi kira ga ofisoshin diflomasiyya da ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da su gaggauta shiga tsakani ta hanyar amfani da tasirinsu, rahoton Blueprint ya tabbatar.











