Ofishin Jakadancin Faransa a Haiti ya ce ƙungiyoyin ƴan daba sun taimaka wa fursunoni wajen tserewa daga gidan yarin da ke baban birnin kasar.
A jiya Asabar da daddare ne gidan yarin Port au Prince mai dauke da fursinoni kusan 4,000 ya fuskanci hari, lamarin da ya sa fursunoni masu yawa suka gudu, ciki har da wadanda suka kashe shugaban kasa.
Ofishin jakadancin ya shawarci masu tafiye-tafiye da su kaurace wa babbanbirnin kasar a halin yanzu.
Hukumar kula da gidajen yarin kasar ta yi kira ga yansanda da sojoji masu motoci da makami su je gidan kurkukun don taimakawa.
Gungun yan daba masu aniyar hambarar da firaiminista Ariel Henry ne ke iko da kashi 80 ba babban birnin kasar haiti.
A ranar Juma’a firaimnistan ya je Kenya don tattauna batun girke dakarun kasa da kasa don kawo karshen karya dokoki a Haiti











