• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

ECOWAS ta magantu akan ficewar kasar Niger, Burkina Faso, Mali daga cikin ta

Sy lawan by Sy lawan
January 29, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Sharuɗɗan da ƙasa za ta cika kafin ficewa daga ECOWAS

Yarjejeniyar da aka kafa ECOWAS a kai ta tanadi wasu matakai waɗanda ake buƙata lallai sai ƙasa ta cika su kafin ta iya ficewa daga ƙungiyar.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

A ranar Lahadi ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka sanar da ficewa daga ECOWAS.

Tun bayan da ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka sanar da aniyarsu ta ficewa daga ECOWAS, jama’a da dama ke ta ce-ce-ku-ce dangane da hakan inda wasu ke tambaya ko shin ƙasashen suna da damar ficewa daga ƙungiyar a duk wani lokaci da suke so.

Tun bayan kafa ECOWAS a 1975, akwai yarjejeniya a rubuce wadda ta zama dokar gudanarwar ƙungiyar bayan shugabannin ƙasashen ƙungiyar 16 sun saka mata hannu, inda aka sake sabunta yarjejeniyar a shekarar 1993 inda shugabannin ƙasashen ƙungiyar waɗanda suka zama 15 daga baya suka saka mata hannu.

Yarjejeniyar ta tanadi abubuwa da dama da suka shafi tsare-tsare da dangantaka da kuma yadda za a gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Babbar tambayar da jama’a suka fi yi a halin yanzu ita ce ko akwai matakai da aka tanada kafin ficewa daga ECOWAS?

A cikin sashe na 91 na kundin yarjejeniyar ECOWAS ta 1993, an tanadi wasu hanyoyi da ƙasa mambar ƙungiyar za bi kafin ficewa.

“Duk wata ƙasa mamba da ke son ficewa daga ƙungiyar za ta bayar da sanarwa a rubuce ga Babban Sakataren ƙungiyar shekara guda kafin ficewar, wanda shi kuma zai shaida wa jihohi mambobi.

“Zuwa lokacin da wa’adin zai kawo ƙarshe, idan ba a janye kudirin ba, ƙasar za ta kasance ta fita daga ƙungiyar,” kamar yadda yarjejeniyar ta ce.

Yarjejeniyar ta tanadi cewa a cikin shekara ɗaya da bayar da wannan sanarwar, akwai buƙatar ƙasar da ke son ficewar ta ci gaba da bin dokoki da tsare-tsaren ƙungiyar kamar yadda yarjejeniyar ta tanada.

Bijire wa ECOWAS

Tun bayan juyin mulki na baya-bayan nan da aka yi a Nijar wanda aka hamɓarar da Shugaba Mohamed Bazoum, ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka ƙara haɗa kansu tare da bijire wa ECOWAS.

Duka ƙasashen uku sojoji ne ke mulkinsu bayan sojojin sun yi wa gwamnatocin farar hula juyin mulki, dalilan da ya sa kenan ECOWAS ɗin ta saka musu takunkumai.

An ta ƙoƙarin sulhu tsakanin ƙasashen da ECOWAS sai dai abin ya ci tura.

Bayan haka ƙasashen sun ƙulla ƙawancen Sahel Alliance ko kuma Liptako-Gourma wadda wasu ke kallo tamkar kishiya ce ga ECOWAS.

Ƙasashen sun ce wannan yarjejeniyar da suka yi za ta mayar da hankali wurin ci-gabansu ta fannin tsaro da tattalin arziki.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Abin takaici, yan bindiga sun dauke Ango da Amarya

Next Post

Kalli dalilan da suka sa aka koma da Danbilki kurkuku

Sy lawan

Sy lawan

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Gioco Responsabile: La Sfida della Sicurezza e della Trasparenza nei Casinò Online

April 21, 2025
Yanzu-yanzu Russia ta magantu kan daga tutar ta da masu zanga-zanga suke a Nigeria

Yanzu-yanzu Russia ta magantu kan daga tutar ta da masu zanga-zanga suke a Nigeria

August 5, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media