• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

ECOWAS ta magantu akan ficewar kasar Niger, Burkina Faso, Mali daga cikin ta

Sy lawan by Sy lawan
January 29, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Sharuɗɗan da ƙasa za ta cika kafin ficewa daga ECOWAS

Yarjejeniyar da aka kafa ECOWAS a kai ta tanadi wasu matakai waɗanda ake buƙata lallai sai ƙasa ta cika su kafin ta iya ficewa daga ƙungiyar.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

A ranar Lahadi ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka sanar da ficewa daga ECOWAS.

Tun bayan da ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka sanar da aniyarsu ta ficewa daga ECOWAS, jama’a da dama ke ta ce-ce-ku-ce dangane da hakan inda wasu ke tambaya ko shin ƙasashen suna da damar ficewa daga ƙungiyar a duk wani lokaci da suke so.

Tun bayan kafa ECOWAS a 1975, akwai yarjejeniya a rubuce wadda ta zama dokar gudanarwar ƙungiyar bayan shugabannin ƙasashen ƙungiyar 16 sun saka mata hannu, inda aka sake sabunta yarjejeniyar a shekarar 1993 inda shugabannin ƙasashen ƙungiyar waɗanda suka zama 15 daga baya suka saka mata hannu.

Yarjejeniyar ta tanadi abubuwa da dama da suka shafi tsare-tsare da dangantaka da kuma yadda za a gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Babbar tambayar da jama’a suka fi yi a halin yanzu ita ce ko akwai matakai da aka tanada kafin ficewa daga ECOWAS?

A cikin sashe na 91 na kundin yarjejeniyar ECOWAS ta 1993, an tanadi wasu hanyoyi da ƙasa mambar ƙungiyar za bi kafin ficewa.

“Duk wata ƙasa mamba da ke son ficewa daga ƙungiyar za ta bayar da sanarwa a rubuce ga Babban Sakataren ƙungiyar shekara guda kafin ficewar, wanda shi kuma zai shaida wa jihohi mambobi.

“Zuwa lokacin da wa’adin zai kawo ƙarshe, idan ba a janye kudirin ba, ƙasar za ta kasance ta fita daga ƙungiyar,” kamar yadda yarjejeniyar ta ce.

Yarjejeniyar ta tanadi cewa a cikin shekara ɗaya da bayar da wannan sanarwar, akwai buƙatar ƙasar da ke son ficewar ta ci gaba da bin dokoki da tsare-tsaren ƙungiyar kamar yadda yarjejeniyar ta tanada.

Bijire wa ECOWAS

Tun bayan juyin mulki na baya-bayan nan da aka yi a Nijar wanda aka hamɓarar da Shugaba Mohamed Bazoum, ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka ƙara haɗa kansu tare da bijire wa ECOWAS.

Duka ƙasashen uku sojoji ne ke mulkinsu bayan sojojin sun yi wa gwamnatocin farar hula juyin mulki, dalilan da ya sa kenan ECOWAS ɗin ta saka musu takunkumai.

An ta ƙoƙarin sulhu tsakanin ƙasashen da ECOWAS sai dai abin ya ci tura.

Bayan haka ƙasashen sun ƙulla ƙawancen Sahel Alliance ko kuma Liptako-Gourma wadda wasu ke kallo tamkar kishiya ce ga ECOWAS.

Ƙasashen sun ce wannan yarjejeniyar da suka yi za ta mayar da hankali wurin ci-gabansu ta fannin tsaro da tattalin arziki.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Abin takaici, yan bindiga sun dauke Ango da Amarya

Next Post

Kalli dalilan da suka sa aka koma da Danbilki kurkuku

Sy lawan

Sy lawan

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Baya ga kayan abinci, kasar Russia ta aike da tallafin motoci makare da makamai ga kasar Niger

Baya ga kayan abinci, kasar Russia ta aike da tallafin motoci makare da makamai ga kasar Niger

April 13, 2024

Responsabilité dans le jeu vidéo : stratégies et enjeux autour de Chicken Road 2

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media