Daga Hassan Umar Gwammaja
Mamba mai wakiltar mazabar Toto da Gadabuke a majalisar dokokin jihar Nasarawa, Mohammed Isimbabi, ya sauya sheka daga jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP zuwa jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Kakakin majalisar, Mista Danladi Jatau, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake karanta wasikar sauya sheka da Isimbabi ya rubuta a zaman da aka yi yau litini
ya ce dan majalisar ya bayyana rabuwar kai a jam’iyyar NNPP a matakin kasa a matsayin babban dalilin da ya sa ya sauya sheka zuwa APC.












