Babban Sufeta Janar, IGP Kayode Egbetokun, ya umarci a tabbatar da tsaron ga duk wanda ya fito zanga zangar da za a yi a watan Agusta
Hakan na kunshe a wata takarda da shugaban ƴan sandan ya aika ga babban lauya mai kare hakkin ɗan adam, Ebun-Olu Adegboruwa
Daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agusta ƴan Najeriya suka tsara gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa da wahalhalun manufofin Tinubu
Ƴan Najeriya mafi akasari matasa sun shirya gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agusta, 2023.
Tun farko dai babban lauyan mai fafutukar kare hakkin ɗan adam, Adegboruwa (SAN) ya rubuta wasika zuwa ga sufetan ƴan sandan, inda ya nemi a ba masu zanga-zanga tsaro.
Lauyan ya rubuta wasiƙar zuwa ga IGP ne a madadin kungiyar Take It Back Movement, ɗaya daga cikin kungiyoyin da za su shiga zanga-zangar a watan Agusta.










