• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

CBN ya musanta cewa ba shi da isassun takardun buga sabon kuɗi

aksam by aksam
February 11, 2023
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Babban Bankin Najeriya CBN ya musanta rahotonnin da ke cewa gwamnan bankin Godwin Emefiele ya alaƙanta rashin wadatattun takardun buga sababbin kuɗi a ƙasar, kan ƙarancin takardun buga kuɗin.

Jaridar PREMIUM TIMES a ƙasar ce dai ta ruwaito wata majiya na shaida mata cewa Godwin Emefiele ya bayyana wa taron majalisar magabatan ƙasar cewa rashin isassun takardun buga kuɗi ne ya haddasa ƙarancin takardun sababbin kuɗin a ƙasar.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

To amma a wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar ya ce babu inda gwamnan banki ya faɗi haka a lokacin da yake yi wa majalisar magabatan jawabi ranar Juma’a a fadar shugaban ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa abin da Mista Emefiele ya faɗa wa majalisar shi ne hukumar da ke lura da buga kuɗin na aikin buga kuɗin domin wadata ‘yan ƙasar da takardun kuɗin da suke buƙata domin harkokinsu na yau-da-kullum.

”Hukumar da ke Lura da Buga Kuɗi ta Ƙasa tana da isassun kayan aikin da take buƙata wajen buga sabbin kuɗin da za su wadatar. Dan haka CBN ke kira ga jama’a da su yi watsi da rahotonnin da ke cewa babu isassun takardun buga kuɗin tare da kiran jama’a su ƙara haƙuri, kasancewar muna bakin ƙoƙarinmu wajen ganin mun ƙara yawan kuɗin da ke yawo a hannun mutane”, in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta ce akwai wani sautin murya da ke yawo a shafukan sada zumunta wanda ke zargin cewa CBN na shirin rufe wasu bankuna a ƙasar, musamman a wasu yankunan ƙasar.

Dan haka sanarwar ta ce CBN ba shi da wannan shiri, kuma saƙon da ke cikin muryar ya saɓa wa dokar tsarin banki na ƙasar.

Dan haka CBN ɗin ya shawarci ‘yan ƙasar da su yi watsi da saƙon sautin muryar kasancewar ba daga bankin yake ba.

Tags: CBNGodwin Emefiele
Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Next Post

Kotun Ƙolin Najeriya ta gargaɗi masu sukar hukuncinta kan Ahmad Lawan da Akpabio

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

CBN ya yiwa yan Najeriya wani babban albishir gameda Dala

CBN ya yiwa yan Najeriya wani babban albishir gameda Dala

February 23, 2024

Die Rolle der Ägyptischen Symbolik in der modernen Esoterik: Ein Blick hinter die Geheimnisse

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media