Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi martani mai zafi kan buƙatar da Atiku ya nemi ta ya yi murabus
Tinubu ya bayyana cewa Atiku har yanzu bai gama warkewa daga ciwon jin zafin rashin nasarar da ya yi a zaɓen 2023 ba
Shugaban ƙasar ya bayyana cewa yana sane da halin da ake ciki kan matsalar tsaro kuma yana bakin ƙoƙarinsa don magance matsalar
Sanarwar hakan ta fito ne daga bakin Bayo Onanuga, mai baiwa Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru.
Sanarwar na cewa: “Maganar da Alhaji Atiku Abubakar ya yi na zargin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da yin tafiyarsa ana cikin ƙalubalen tsaro da tattalin arziki, abu ne da za a kira mara kan gado.
“Hakan na zuwa kwanaki kaɗan bayan ya yi wa shugaban ƙasa ƙazafi a kan batun karɓar lamunin da kamfanin NNPC ya yi, bayanin nasa na baya-bayan nan ya gaza kai abin da ake tsammani daga wajen dattijon ƙasa.
“Muna so mu yi amanna cewa har yanzu Alhaji Atiku bai warke daga shan kayen da ya yi a zaɓe ba, kuma yanzu ya koma neman kafar da zai riƙa kai wa Shugaba Tinubu hari












