Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ya yi magana kan matsalar rashin tsaronda ake fama da ita a ƙasar nan
Ribadu ya bayyana cewa yawaitar ƙanaanan makamai da cin hanci a bangaren tsaro su ne manyan dalilan da suka haddasa rashin tsaro a ƙasar nan
Ya yi nuni yadda gwamnati mai ci ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta samu nasarori a fannin samar da tsaron a fafutukar da ta ke yi Tun bayan kafuwarta
A cewar sa gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki matakai da dama domin rage yawaitar ƙananan makamai wanda a cewarsa ya samar da sakamako mai kyau, rahoton jaridar Premium Times ya tabbatar.











