Kimanin yara takwas sun rasa ransu bayan da ƙasar gini ta rufta musu a mahaƙar ƙasar gini.
Lamarin ya afku ne a Dustin Dukku da ke unguwar Badariya ƙaramar hukumar Birnin Kebbi.
Shugaban ƙaramar hukumar mulkin ta Birnin Kebbi Hon. Muhammad Dahiru Ambursa, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai , inda ya ce tuni aka fara shirye-shiryen yi wa yaran jana’iza.
Ya kuma ce akwai wasu ƙarin yara biyu da suka jikkata ciki har da wanda ya karye a ƙafa.
Kazalika ya ce mafi yawa daga cikin yaran da lamarin ya rutsa da su almajirai ne waɗanda ke aikin haƙar ƙasar gini a yankin












