Rukuni na hudu, mai ɗauke da ɗalibai 150 da gwamnatin Kano mai ci ta dauki nauyin karatunsu a ƙasashen ketare sun tashi zuwa ƙasar India domin yin karatun digiri na biyu a fannoni daban-daban.
Masana na bayyana hakan a matsayin daya daga cikin manyan alkawura da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi a lokacin yakin neman zaben sa, inda bayan ya hau mulki, ya dauki nauyin ƴan asalin jihar Kano su dubu 1,100 domin kai su ƙasashen waje su yi digiri na biyu.
Tuni bayan karbar rantsuwa aka fara shirin inda a yau Juma’a rukuni na huɗu ya tashi zuwa kasar India daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano, da misalin ƙarfe 7:30 na safe.
Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan tashin ɗaliban, Kwamishinan Ilimi mai Zurfi na jihar, Dr Yusuf Kofar mata, ya ce za su sauka a Legas ne kafin su wuce zuwa India.
A cewar sa, da saukar su a India, za a kwashe su zuwa jami’o’i daban-daban da za su yi karatun su a fannonin ilimi daban-daban.
Ya kara da cewa Tallafin karatun na daya daga cikin manya-manyan alkawura da Gwamna Yusuf ya dauka kuma ya ke cika su tun ba wanda kujerar mulki a jihar.
Dr Kofarmata ya kuma yi nuni da cewa ɗaliban da iyayen su na cike da farin ciki da godiya ga Gwamna Yusuf bisa wannan tagomashi, inda ya yi kira gare su da su dage su yi karatu su kuma zama wakilan jihar da ma Nijeriya baki daya a ƙasashen da aka kai su.












