Tun bayyan kammala zabin jahohin Bayelsa da Imo da kuma Kogi’yan siyasar suke ta tufa albarkacin bakinsu a sakamakkon amfani da makodin kudade wajan siyan kuri’un jama’a
A cewar Shehu Sani Jami’an tsaro sun kama wasu ‘yan siyasa a ranar Asabar bayan da aka kama su da makudan kudade, ana zarginsu da sayen kuri’u.
Kwamared Shehu , ya kuma kara dacewa idan kasar ta ci gaba da tafiyar da tsarin dimokuradiyya da ke karfafa sayen kuri’u, masu kudi ne kawai za su ci gaba da mulki.
Sanarwar ta ci gaba da cewa,matukar za mu gudanar da tsarin dimokuradiyya wanda zai karfafa tare da amincewa da yin amfani da kudi wajen siyan kuri’un wakilan jam’iyya da kuma sayen kuri’un al’umma.
To zabe a Nijeriya zai kasance ne kawai ga mutanen da za su iya zuba kudadensu su sayi kuri’u ba tare da wata matsala ba.










