• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
August 30, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

AKSAMMEDIA KANO — A lokacin da tsarin samar da fasfo ke fuskantar sauyin daga Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya (NIS) ta ce yana da nufin mayar da aikin buga littafin fasfo zuwa cibiyar Abuja, lamarin ya jawo sabon tambaya daga Arewa: ina muryar waɗanda aka zaɓa domin kare muradun al’umma?

Sheikh Muhammad Nasir Yahya ya yi wannan tambayar ne a hudubar Juma’ar da ya gabatar a Masallacin Juma’a na Sasif da ke Unguwar Gwagwarwa, Ƙaramar Hukumar Nassarawa a Kano, inda ya bayyana matakin da ya shafi wasu cibiyoyin fasfo a matsayin wani ƙalubale da ya kamata shugabannin siyasa da wakilan jama’a su duba da muhimmanci.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Malamin ya ce idan har yankunan Arewa sun samu kaso mai yawa daga cikin cibiyoyin da aka shigar da su cikin sabon tsarin, ya kamata gwamnonin Arewa, sanatoci da ’yan Majalisar Wakilai su tashi tsaye domin kare muradun al’ummar da suka zaɓe su. Ya tunatar da su cewa rantsuwar da suka yi da Alƙur’ani Mai Girma lokacin karɓar amanar wakilci ba abin ado ba ce, illa nauyi ne da ya kamata ya bayyana a aikace.

Ya kuma jefa tambaya mai nauyi ga wakilan jama’a: “Idan aka ɗauki matakin da zai iya ƙara wa jama’a wahala, amma waɗanda aka zaɓa domin kare muradunsu suka yi shiru, shin wannan ba alamar gazawar wakilci ba ce?”

Sai dai NIS ta jaddada cewa ba ta rufe ofisoshin karɓar bayanan masu neman fasfo ba; abin da aka sauya shi ne tsarin production/personalisation, inda ake samar da littafin fasfo a cibiyar Abuja, yayin da cibiyoyin yankuna ke ci gaba da karɓar bayanan biometric na masu neman fasfo.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Shettima Ya Nemi Kada A Yi Masa Tallan Taya Murna Kan Cikarsa Shekara 60

Next Post

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Shettima Ya Nemi Kada A Yi Masa Tallan Taya Murna Kan Cikarsa Shekara 60
LABARAI

Shettima Ya Nemi Kada A Yi Masa Tallan Taya Murna Kan Cikarsa Shekara 60

by Khadija Maitaya
August 29, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Wasu Yan jam’iyar APC na nuna kosawar su da jagorancin Ganduje

Wasu Yan jam’iyar APC na nuna kosawar su da jagorancin Ganduje

January 21, 2024
Tsokacin masana gameda karfin tattalin arzikin kasar Russia

Tsokacin masana gameda karfin tattalin arzikin kasar Russia

March 19, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media