Shugaban dilllan rimin zakara alhaji naziru annatija shine yabaina koken Yan qungiyar kan yanda gwamnatin jihar Kano keyimusu wasa da hankali tare da hadasu rigima da da abokanan cinikaiyarsu.
Anasa jawabin guda Daga cikin dilllan garin ishaq Abba shawus yace basa barci sakamakon yanda kwamishina yakeneman hadasu rigima da mutanen dasuka siyarwa da filayen, kamar yanda kwamishinan yaibayani agidajen Radio cewa anbiya diyar garin rimin zakara inda suka bayyana wannan zance bahaka yakeba domin kuwa ba abiyasu ko sisiba illa qoqarin kwacewa al’umma dake da qaramin qarfi fulotansu.
Shima alhaji sulaiman dangadi Wanda shine shugaban bangaren rijiyar zaki yaroqi gwamnan jihar kano Alhaji Abba kabir Yusuf dayadubi Allah yabinciki yanda kwamishinan qasa yakeyiwa alumnar garin rimin zakara domin ita gwamnati raba rigima akasanta da ita ba hada rigimaba.
Dayawa daga ma mallaka filaye agarin rimin zakaranne sukayi batutuwan dasukashafi fulotannasu inda suka baiyana Rashin qarfinsu da Neman Taimakon gwamna kan Neman durqusardasu da kwamishina yakeneman yi.










