• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda makarantu 22 suka rabauta ta tagomashin kayan koyar wa a karamar hukumar Dawakin Tofa

aksam by aksam
January 11, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
476
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Musa Mudi Dawakin Tofa

DETFund: Ya Raba Tallafin Kayan Koyarwa ga Makarantu 22, a Dawakin Tofa.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Asusun Tallafawa Ilimi na Dawakin Tofa (Dawakin Tofa Education Trust Fund DETFund) ya gabatar da taron raba tallafin kayan koyarwa ga makarantu biyu-biyu daga mazabu 11 a karamar hukumar, don kara bunkasa harkokin ilimi, a ranar Asabar 11/01/2025.

Shugaban kwamatin kula da asusun DETFUND Dr Junaidu Dalladi ya ce an samar da asusun ne a karkashin kulawar kungiyar Malaman Makarantun Gaba da Sikandire ‘Yan Asalin Karamar Hukumar Dawakin Tofa (Dawakin Tofa Academic Forum DAF), tun a shekara ta 2023, don taimakawa da bunkasa harkokin ilimi a ciki da wajen karamar hukumar.

“… Tun bayan da kungiyar DAF ta samar da kwamatin wannan shi ne karo na biyu da asusun ya raba tallafin kayan koyarwa ga makarantu 22 dake karkashin hukumar kula ilimin bai daya ta Dawakin Tofa”.

“… An raba katan 3 na kwallin alli da littafin rubutu 40 da littafin adana bayanan koyarwa 4 da rigistar kiran suna 4 ga kowacce makaranta”.

“… Ya yi kira ga sauran al’umma da su rika bada tallafinsu don kara ciyar da harkokin ilimi gaba a karamar hukumar”.

Shugaban kungiyar DAF Associate Professor Engr. Mamunu Mustapha Imam ya godewa duk mutanen da suka sanya tallafinsu a cikin asusun don ganin an kara bunkasa harkokin ilimi a karamar hukumar Dawakin Tofa.

Sakataren ilimin hukumar bai daya ta Dawakin Tofa Malam Ahmad Shu’aibu ya yabawa kokarin kungiyar DAF kana ya yi kira ga makarantun da suka amfana cewa sun yi amfani da tallafin ta hanyar da ta dace da kuma sanyasu a inda suka dace.

Shugaban kwamatin bada tallafin karatu na karamar hukumar Dawakin Tofa Malam Abdullahi Mijinyawa ya bukaci kungiyar DAF da ta fadada neman tallafin DETFund ga sauran al’umma musammanma masu daukar albashi.

Sakataren gidauniyar ilimi ta Sale Kuidawa Malam Lawan Usman Dawaki ya yi alkawarin cigaba da baiwa kungiyar DAF hadin kai akodayaushe, kana ya bukaci kungiyar da ta rika rubutawa shugaban gidauniyarsu sakon neman taimako a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

Kansilan riko a sashen Ilimi na karamar hukumar Dawakin Tofa Honarabul Muhammad Ahmad da hedimastoci 22 na daga cikin wadannan suka halarci taron raba tallafin DETFund, a cikin dakin taro na cibiyar gudanar da harkokin addinin Musulunci dake Dawakin Tofa a jihar Kano.

Share190Tweet119SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Tsohon Kwamishinan Gwamnan Kano Ya Chanja Sheka Da NNPP Zuwa APC

Next Post

Sakon Bangajiya:- Ango Abdullahi Bala Abbas

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Analisi Strategica dei Giochi di Fatica e l’Impatto sul Benessere dei Videogiocatori

April 23, 2025

F7 Casino Slot Games: Tips for Beginners

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media