Daga Hassan Umar Gwammaja
Jami’in yaɗa labarai na rundunar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya shaida wa manema labarai a lokacin da ya ke gabatar da waɗanda ake zargi da aikata laifin.
Ya ce, Abubakar Mohammed Kabir daga Kaduna, da mannir Musa daga Dutsinma da kuma Aliyu Iliya daga Safana sun yi ƙokarin kai albarusan ne ga ƙasurgumin ɗan bindiga mai suna Harisu a dajin Yauni da ke ƙauyen Ummada a ƙaramar hukumar Safana.
ASP Sadiq ya ƙara da cewa, su waɗannan miyagun mutanen tuni suka amsa laifinsu tare da cewa sunyi safara albarusan ne daga jihar Nassarawa.
Ya ce, nan ba da jimawa ba da zarar sun kammala bincike za a gurfanar da masu laifin a gaban ƙuliya.












