Bukin yaye daliban da raba kyaututtuka na dalibai dari da tamanin da suka hada da matakin na farko na share fagen firamare da matakin firamare da karamar sakan dare da kuma babban sakandare.
An gudanar da a taron a sabuwar jami’a Bayero Wanda ya samu halattar manyan baki da mashahuran masana a fannin ilmi da iyayen Yara.
Dr Muhammad Adamu kwankwaso ya yaba da himma da kwazon daliban makarantar tare dayin Kira ga malaman makarantar dasu rubanya kokarisu wajen tatbiyya domin karatun baya samun nagarta muddin ba,a hadasu wuri guda da tarbiyya
Farfesa Khadija Hafiz tayi Kira ga daliban da cewa duk da sun samu ilmin su hada da sa,na’a don Kar su zauna haka domin shi rashin sana,a illa ne ga matasa.
Daraktar makarantar Hajiya Surayya Husain Lawan ta bayyana gagaruma nasarar da makarantar ta samu a sakamakon jarrabawar sakamdare da ta gabata tare da godewa mahalatta taron da damar da suka bawa wannan taron suka halatta da Kuma fatam mahalicci ya Mayar da kowa gida lafiya.











