• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Bazoum, Kotu ta baiwa shugaban kasar Niger zazzafan umarni

aksam by aksam
April 4, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Wata kotu a birnin Yamai ta umurci hukumomin tsaro a jamhuriyar Nijar su gaggauta sakin wasu makusantan hambararren shugaban kasa Mohamed Bazoum daga inda ake tsare da su.

Alkalin kotun yace ana tsare da wadanan mutane ne ba akan ka’ida ba kuma jinkirin mutunta wannan hukunci abu ne da zai ja wa gwamnatin kasar biyan tarar miliyan 1 na cfa a kowace rana har zuwa lokacin da za a bai wa wadanan mutane damar komawa cikin iyalinsu.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Tun a ranar da hukumomin mulkin sojan Nijar suka zargi hambararren Shugaban kasa Mohamed Bazoum da yunkurin tserewa daga inda yake tsare ne jami’an tsaro suka kama Abdourahamane Ben Hamey da Mohamed M’Barek a jerin mutanen da ake zargi da hannu a abinda aka kira yunkurin tada hankalin kasa da yi wa hukuma barazana.

An ja lokaci mai tsawo ba tare da jin duriyar wadanan mutane ba kafin daga bisani a gano cewa suna tsare a wani ofishin jamia’n tsaron Jandarma dake birnin Yamai lamarin da ya sa lauyoyinsu shigar da kara a kotu domin ta dubi abin da suka kira take doka da tauye hakkin bil adama.

Bayan nazari akan bahasin bangarorin biyu a zamanta na talata 2 ga watan Afrilu, kotun ta umurci hukumomi su salami wadanan mutanen.

Yace Doka ta kayyade cewa bai kamata a fice wata 1 a na tsare da mutun ba tare da an gabatar da shi gaban alkali ba. su kuma wadanan mutane sun shafe watanni 6 da mako 2 a ofishin jandarmomi abin da ke nufin ana tsare da su ne ba akan ka’ida ba.

Domin tabbatar da cewa an bi umurnin Kotun alkalin dake wannan shari’a ya gindaya wa mahukunta sharadi inji Maitre Djibo.

Yace za ta yiwu hukumomin Nijar su yi ta jan kafa kokuma su ki zartar da hukuncin kotun. matakin da ke biyo bayan aikata wannan dabi’a ta kin sakin wadanan mutane shine biyan tarar miliyan 1 na cfa a kowace rana har zuwa lokacin da komai zai je daidai.

Kawo yanzu ba wani martani daga bangaren gwamnatin Nijar wace ma’aikatar Agence Judiciare de L’etat ke wakilta a wannan shara’a koda yake hukuncin kotun na cewa akwai damar daukaka kara kafin nan da makwanni biyu masu zuwa.

A saurari cikakken rahoton Souley Moumouni Barma:

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda kungiyar IS ta kai mummunan hari a wata kasar Africa

Next Post

Shugaba Tinubu Zai Bar Abuja A Gobe Lahadi Zuwa Legas Don Yin Bikin Karamar Sallah

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Pandabet Casino’s Payment Processing Times Explained

April 21, 2025
Nadin sarauta, Sarkin Gaya ya yi wa ta Lawan abin da ya kamace su

Nadin sarauta, Sarkin Gaya ya yi wa ta Lawan abin da ya kamace su

October 9, 2023
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media