Wasu ƴan bindiga sun yi awon gaba da ɗalibai masu tulin yawa a yankin Evwreni da ke titin Gabas maso Yamma a Ughelli ta jihar Delta.
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya tattauna da sarakunan unguwar Dorayi kan rikicin daba da ya kunno kai a baya-bayan nan.
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya bai wa maniyyata jihar kyautar Naira miliyan daya kowannensu, biyo karin kudin kujerar aikin hajjin bana.
Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta ciyo bashin naira biliyan 14.26 sai dai kuɗin wani ɓangare ne na kuɗaɗen da gwamnatin da ta shuɗe ta ciyo na naira biliyan 20.
Wani saurayi da ya kamu da tsananin kaunar wata budurwa, Hauwa Abatcha Ngala dukkansu daliban Jami’ar Maiduguri, ya yi mata mummunan rauni a kai tare da barazanar kasheta saboda kin amincewa da soyayyarsa.
Mahaifi ya kai ɗansa kara ofishin ƴan sanda bisa zargin satar baburan mutane a Kaduna.
Rundunar ƴan sandan ƙasar Ghana ta ce ta karɓo wata yarinya ƴar shekara 12 da ake zargi wani malamin cocin gargajiya mai ƙarfin faɗa aji ya aura a ƙarshen makon jiya.
An dakatar da aikin ceto masu haƙar ma’adinai da suka maƙale a Rasha.
Yau ake rantsar da sabon shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye.
Rikicin kabilanci ya sake hallaka wasu mutane 23 a kudancin Chadi.
Dubban Isra’ilawa ne sunyi zanga zanga a majlisar dokokin ƙasar inda suka buƙaci gwamnati ta yi sulhu da Hamas don musayar fursunoni tare da neman a gudanar da sabon zaɓe cikin gaggawa.
Isra’ila ta kashe wani babban kwamandan dakarun juyin-juya-halin Iran a ƙasar Syria.
Isra’ila ta kori kafar Talabijin ta Al Jazeera daga kasarta.
Kocin Bunley Kompany yace alkalancin wasanni ya samu gagarumar koma baya a Ingila.
Alan Shearer yace yana da kwarin gwiwar Manchester City za ta lashe kofin Firimiya a bana.












