Yayin da aka shafe shekara guda da faruwar iftila’in tagwayen girgizar kasar da ya wakana a watan Fabrairu shekarar da ta Gabata ta 2023, Turkiyya ta gudanar da bukukuwan nuna alhini da Girmamawa ga wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka tsira a fadin kasar.
Turkiyya ta gudanar da jimamin tuna girgizar kasar ta ranar 6 ga watan Fabrairun 2023, wadda ya afku a kudancin kasar, inda ta yi sanadiyar mutuwar mutum 53,537 tare da jikkata wasu fiye da 107,000.
Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 7.7 da 7.6 ta afku ne a larduna 11 na kasar ta Turkiyya.
Sama da mutane miliyan 14 ne girgizar kasar ta shafa a kasar Turkiyya, da kuma wasu da dama a kasar Syria.
Mutane a faɗin ƙasar ciki har da na yankunan da aka yi girgizar ƙasar, sun gudanar da tarukan jimamin don tunawa da wadanda suka mutu a bala’in.
An yi shiru na ɗan lokaci da misali ƙarfe 4.17 na asubahin ƙasar, daidai lokacin da masifar ta faru.
A nasa jawabin shugaban kasar Turkiyya raciep Tayyip Erdogan ya ce gwamnatin kasar na aiki tukuru don cika alkawuran da ta yi wa al’ummar kasar, inda ya kara da cewa: “Zai ci gaba da wannan kokari har sai ya gina da kuma farfado da garuruwan da abin ya shafa.”
Kana shugaban zai halarci wani taro a birnin Kahramanmaras na bai wa wasu daga cikin waɗanda suka tsira daga iftila’in sabbin gidajen zama.
Shi ma Ministan Harkokin Wajen kasar Hakan Fidan ya yi taron jimamin tunawa da girizar ƙasar da waɗanda suka rasa rayukansu.
Ya wallafa a shafin X cewa “Za mu ci gaba da tsayawa ƴan ƙasarmu,” kuma ya gode wa ƙasashen da suka tsaya kai da fata tare da kasar Turkiyya a lokutan da ta fuskanci iftila’in.
Karshen rahoton kenan Abubakar Sulaiman Gwammaja a zare da Abawa












