Dan takaran Shugaban Kasa a karkashin tutar babbar jam’iyar adawa ta NDC a zaben 2024, kuma tsohon Shugaban Kasa, John Dramani Mahama, ya ba da tabbacin cewa, a shirye yake ya ba Musulman kasar karin hutun bukukuwan Idi, idan jam’iyarsa ta samu nasara a zabe mai zuwa.
Tsohon Shugaban Kasar ya bayyana hakan ne a taron shekara shekara na kungiyar Ghana Muslim Mission karo na 63 a birnin Kumashi, inda ya jaddada bukatar gyara Dokar Hutun Jama’a na 2001.
Yace: “Aniyarmu ce mu warware matsalar da wasu ‘yan uwa musulmi da ba sa jin dadin hutun jama’a na karshen azumin watan Ramadan saboda dokar kwanaki 29 ko 30, na ganin watan. Don haka, za mu kara hutu a cikin bukukuwan Eid-el-Fitr.
“Insha Allahu idan an zabe mu, za mu kara hutu a bikin Eid-el-Fitr. Kuma za mu yi hakan ne ta hanyar sake fasalin Dokar Hutu ta Jama’a ta yadda Ghana za ta ci gaba da gudanar da bukukuwan hutu iri daya a kowace shekara”, a cewarsa.
Garba Osman, dan jarida kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, ya bayyana jin dadinsa ga wannan alkawari duk da cewa wasu na ikirarin cewa domin siyasa ne ya yi wannan alkawarin.












