Gwamnatin jihar Enugu ta ce babban matsalar da su ke fuskanta a jihar itace ta sautukan dake fitowa daga wuraren ibada cikin dare a fadin jihar.
Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa Gwamnatin ta ce ya zama wajibi Mujami’u da Masallatai su sanya sinadaran da za su hana sauti fita daga wuraren ibadun su saboda yadda suke hana jama’a bacci da daddare.
Shugaban hukumar raya birane na jihar Uche Anya ne ya sanar da haka lokacin da yake bayanin matakan da su ke dauka domin kare ‘yancin jama’a.
Anya ya ce abin takaici ne yadda wuraren ibadun da kuma gidajen rawa ke hana jama’a bacci wajen gudanar da harkokin su cikin dare.
Jami’in yace ba za su lamunci irin wadannan sautukan da ke hana jama’a bacci cikin dare da sunan ibada ba, saboda haka za su dauki kwararan matakan da suka dace a kai.
Anya ya kuma ce duk wani gidan da aka gina ba bisa ka’ida ba a biranen jihar zai gamu da fushin hukuma.












