Jihar Nasarawa – Rundunar ƴan sandan jihar Nasarawa ta cafke wasu mutum 10 bisa zargin satar yara da sayar da su.
Shehu Nadada, kwamishinan ƴan sandan jihar ne ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar da ke birnin Lafia a ranar Juma’a, cewar rahoton TheCable.
Kwamishinan ya ce jami’an ƴan sandan da ke aiki da sashen Keffi, a sintiri na yau da kullum a ranar 10 ga watan Janairu, sun ceto wani mutum daga masu shirin yi masa taron dangi.
Da aka gudanar da bincike, an gano cewa ana zargin mutumin da sace wani yaro ɗan shekara biyar a Keffi, rahoton jaridar Vanguard ya tabbatar.
Nadada ya ce daga baya wanda ake zargin ya amsa laifin cewa shi mamba ne na ƙungiyar da ta ƙware wajen satar yara da sayar da yara ga manyan ƴan kasuwa.
Ya ce binciken da aka yi ya kai ga kama wasu mambobin ƙungiyar mutum tara.
Ya ƙara da cewa binciken da aka yi a wayoyinsu ya nuna cewa sun yi awon gaba da yara 45 sun sayar da su, waɗanda aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar nan.












