• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Sema ta fitar da sabon adadin wadanda suka mutu a harin Gwoza

aksam by aksam
June 30, 2024
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Borno (SEMA) ta ce mutum 18 ne suka mutu a harin bom da wasu da ake kyautata zaton ‘yan ƙunan ɓakin wake ne suka tayar a wurin taron biki ranar Asabar a Gwoza da ke jihar.

Cikin rahoton aukuwar lamarin da hukumar ta fitar, babban daraktan hukumar, Barkindo Saidu ya ce mutum 48 ne suka samu munanan raunuka a harin, wanda ya kasance ɗaya daga cikin mafiya muni a baya-bayan nan.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Shugaban hukumar Barkindo Saidu ya fitar ya ce “A gaban idona, da misalin ƙarfe 3:00 na rana, bom na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata mace ta tayar bayan ta kutsa cikin taron bikin”.

Bayan tashin bom na farko, wanda ya jikkata fiye da mutum 30, tare da kashe wasu, sai na biyu ya sake tashi a kusa da babban asibitin yankin, in ji Barkindo Saidu.

”A yayin da mutane ke yi wa waɗanda suka mutu jana’iza, sai bom na uku ya tashi, inda nan ma wata mace ta tayar da shi tare da kashe wasu”, in ji daraktan na SEMA.

Ya ƙara da cewa bom na huɗu ya fashe ne a asibiti, wanda wata matashiya ta tayar a lokacin da jami’an hukumar da likitoci ke taimaka wa waɗanda hare-haren farko suka jikkata.

“Kawo yanzu mutum 18 ne suka suka mutu, da suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara da mata masu juna biyu. Mutum 19 da suka samu munanan raunuka an kai su babban asibitin Maiduguri domin basu kulawar gaggawa” in ji Saidu.

Ya kuma ce akwai wasu ƙarin mutum 23 da ke jiran rakiyar sojoji domin kai su asibitin.

Tuni dai sojoji suka sanya dokar hana fita a faɗin ƙaramar hukumar Gwoza, sakamkon hare-haren.

 

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

A Yau Lahadi Ne Za a Gudanar Da Bikin Dauren Auren; Babban Kwamandar Wanzar Da Zaman Lafiya Na Jihar Kano

Next Post

Dalilan SERAP na neman cikakken bayanin biliyan 100 daga gwamnan CBN

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Kotun Daukaka Kara Dake Zamanta a Abuja Ta Tabbatar Da Nasarar Zaben Gwamna Bala Muhammed Na Jihar Bauchi

August 6, 2024
Wani Farfesa ya fadi abin da zai faru idan Tinibu ya gaza shawo kan tsadar rayuwa a Najeriya

Binciken Dala 6m da aka sata da sahanun Buhari ya canza salo

February 20, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media