Daga Hassan Umar Gwammaja
Kamar yadda da yawa daga cikin al’ummar kasa suka aani, tuni aka fara amfani da tsarin INTERNET na *5G* Najeriya.
Sai dai a halin yanzu ‘yan danfara ta INTERNET sun fara kiran mutane suna bukatar jama’a da su mayar da layukan su zuwa 5G.
Suna yin haka ne ta hanyar kiran mutum su ce masa za’a tura masa da wasu lambobin sirri da ake kira da *OTP* su ce ya tura musu wadannan lambobi domin inganta masa layinsa na SIM Card.
Da zarar mutum ya yi kuskuren tura musu wadannan lambobi nan take za su samu shiga asusun bankinsa (Bank account) su kwashe duk kudinsa su tura zuwa na su asusun.
Don Allah a kiyaye kar ku bari wani mutun ya yaudare ku ta hamyar sanya ku tura masa wadansu lambobi.
Idan kuna da wani kokonto ku ziyarci bankin ku kai tsaye.
Sanarwa da hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC).












