Ƴan bindiga sun yi awon gaba da mutane 20 a samamen da suka kai Abuja
Ƴan bindiga sun yi awon gaba da wasu mutane 20 a unguwar Dawaki da ke kusa da yankin Kubwa a babban birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, biyo bayan wani samame da suka kai.
An kashe uku daga cikin maharan yayin da aka kama biyu daga cikin su.
An kashe uku daga cikin maharan yayin da aka kama biyu daga cikin su. © dailytrust
Da:
Majiyoyi sun ce maharan, waɗanda suka kai kimanin 50, sanye da khakin soja, sun kai harin ne a layin Frank Okpara, kafin daga bisani jami’an tsaro su taka musu birki, sakamakon kiran gaggawa da aka musu.
Shugaban wannan al’umma ta Dawaki Rock Heaven Community, Tunde Abdulrahim, ya ce lamarin ya auku ne bayan almuru a Lahadi, inda maharan suka kutsa unguwar da muggan makamai dabam-dabam.
Wannan lamari na zuwa ne jim kaɗan bayan da ƴan bindiga suka kai farmaki Shagari Quaters a yankin Dei-Dei na, wanda ke kan titin Kubwa zuwa Abuja, inda suka yi awon gaba da iyalin wani jami’in kwastan.
Wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce ƴan bindigan sun sace mmutane 17 daga gidaje 3 a layin; sai dai ya ƙara da cewa, 5 daga cikin waɗannen mutane sun tsere a yayin da ake tafiya da ssu zuwa wani tsauni a wajen yankin.
Rahotanni sun ce a yayin da yan binidga suka kama hanyar wani gandun daji da ke kusa da madatsar ruwa na Usuma, sun gamo da jam’i’an DSS, inda suka yi artabu.











