Matasan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Edo sun fantsama cikin zanga-zangar lumana yau Litinin, 19 ga watan Fabrairu, 2024.
Matasan sun yi wannan zanga-zanga ne kan abinda suka kira mulkin kama karya na kwamitin ayyukan APC na jihar Edo (SWC).
Masu zanga-zangar sun yi kira ga uwar jam’iyyar APC ta ƙasa karƙashin jagorancin Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ta rushe shugabancin jam’iyya na jihar.
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, matasan sun buƙaci a rushe SWC domin zaman lafiya ya samu gindin zama a jam’iyyar kuma a tunkari abinda ke gaba.
Sai dai matasan APC na jihar Edo sun jinjina tare da yabawa shugaban kwamitin zaben fidda ɗan takarar gwamna kuma gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma.
Sun yabawa Uzodinma ne bisa ayyana wakilin mazaɓar Ovia a majalisar wakilan tarayya, Dennis Idahosa, a matsayin sahihin ɗan takarar gwamna a zaɓen jihar da ke tafe.












