Kungiyar masu hada hadar kasuwancin wayoyin hannu dake kasuwar bata ta jaddada aniyarta na hada hannu da ma’aikatar kasuwanci da ciniki ta jihar Kano domin bunkasa harkokin kasuwancin ‘ya’yanta a fadin jihar Kano.
Sakataren janar na kungiyar Alh Aminu Uba Wada ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da Manema labarai a ofishinsa dake karami plaza.
Sakataren yace Kungiyar ta dauki gabaran bin dukkannin hanyoyin da suka dace domin ganin ta bijiro da sabbin abubuwan da za su infanta kasuwancin alammar kasuwar wayoyin hannu.
Aminu Uba Wada yace lokaci yayi da ya kamata masu sana’ar wayoyin hannu na kasuwar bata su San Yadda Ake gudanar da shugabancin da Ake yi musu Wanda za’a yi sa a Bude ba kamar Yadda sauran shugabannin Baya suka yi ba.
Sakataren yace wannan shugabanci suke yi Yanzu, Shugabanci ne na riko Wanda da zarar lokacin zabe yayi jagororin za su sauka daga kan shugancin tare da gudanar da sahihin zabe domin ciyar da alummar kasuwar gaba.
Sakataren janar na kungiyar ya bayyana cewar, mutane su tuna cewa gudanar da kasuwanci ba Yana nufin Wanda yake jagoranci ya zo domin azurta kansa bane, ya zo ne domin hidimtawa al’umma.
Shugabannin Baya da suka jagoranci kasuwar, sun mayar da shugabancin sai Yadda suke so Wanda Yanzu Kuma ba haka bane, saboda Yanzu alummar kasuwar suna da ‘yancin fadar albarkacin bakinsu.
Haka zalika sakataren Kungiyar yayi Kira ga dukkannin ‘ya’yan Kungiyarsa da su baiwa jagororin cikakken hadin Kan daya kamata domin Samar da kyawawan Shugabanci a ciki da wajen kasuwar.
Daga karshe sakataren yace za su yi duk maiyiyuwa wajen ganin sun baiwa Gwamnatin jihar Kano cikakken goyan bayan da suka dace domin ciyar da kasuwancin jihar Kano da al’umma gaba, Inda yace yin hakan zai sanya jihar Kano ta yi gogayya da sauran kasashen Duniya ta fannin kasuwanci.












