Daga Hassan Umar Gwammaja
A ranar Alhamis ɗin nan data gabata ne dai Hukumar NEMA ta bayyana halin da ake ciki game da irin ta’adin da ambaliyar ruwa ta haifar a sassan Najeriya, inda ta ce akalla kadada dubu 107,652 ta shafe, ta kuma lalata gidaje dubu 80,049.
Daga cikin jahohin da iftila’in ya shafa akwai jihar Ribas da Neja da Benue da kuma jahohin da dama da ke yankin arewacin Najeriya.
A ziyarar da shugaban ma’aikatan fadar Shugaban kasa Femi Gbajabiamila ya kai ofishin Hukumar NEMA, Darekta Janar na hukumar, Zubaida Umar, ta ce NEMA ta gudanar da bincike a kusan dukannin jahohin ƙasar dangane da iftila’in, sannan ta ƙara da cewa rashin samun tallafin kuɗi ne babbar matsalar da ke shafar aikin hukumar.












